Niger

Nijar :Kasar Senegal na rokon shugaban kasar Nijar da ya saki tsohon shugaban kasar M.Tandja

Mamadou Tandja tsohon Hambararen shugaban kasar Nijar.
Mamadou Tandja tsohon Hambararen shugaban kasar Nijar. RFI/Christine Muratet

Shugaban kasar senegal Abdoulaye Wada a lokacin da ya ke karbar sakon fatan alheri daga shugaban kasar Nijar Salou Djibo,dangance da bikin al’adun al’ummomin bakaken fata na duniya da ke gudana a Dakar babban birnin kasar ,ya nemi shugaban da ya saki tsohon shugaban kasar Mamadou Tandja . Wanan kir aya so daidai da hukumcin da kotun kungiyar kasashen tattalin Afrika ta Yamma CEDEAO ko kuma ECOWAS ta yanke a zamanta a garin Abuja a tarrayar Najeriya.