Zanga-zanga don nuna adawa da Boko Haram a Nijar
Kawancen jam’iyyun da ke kan karagar mulkin Jamhuriyar Nijar ya bukaci al’ummar kasar baki daya da su gudanar da zanga-zangar nuna goyon baya ga gwamnatin kasar wadda ta kuduri aniyyar fada da mayakan Boko Haram da suka soma kai wa kasar hare-hare.
Wallafawa ranar:
Jam’iyyun siyasar sun bukaci a gudanar da wannan zanga-zanga a ranar 17 ga wannan wata na Fabarairu a duk fadin kasar.
Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da shugaban kasar Mahamadou Issifou ya bukaci al’ummar kasar da su mara wa sojoji da kuma sauran jami’an tsaron kasar baya a kokarin da suke na kare iyakokin kasar daga barazanar wannan kungiya.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu