Kotu ta tantance mutane 15 domin takarar shugabancin Nijar
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Kotun Tsarin Mulki a Jamhuriyar Nijar ta wanke mutane 15 daga cikin 16 da ke nemnan tsayawa takarar shugabancin kasar a zaben da za a yi ranar 21 ga wata Fabarairu mai zuwa.
Daga cikin mutanen da kotun ta tantance d akwai shugaban kasar mai-ci Alhaji Issoufou Mahamadou, da jagoran ‘yan adawa na kasar Alhaji Seini Oumarou, da Hamma Amadou wanda yanzu haka ke tsare a gidan yari bisa zargin sayo jarirai daga Najeriya.
Har ila yau kotun ta wanke daya daga cikin mutanen da ake zargi da hannu a cinikin jariran mai suna Abdou Labo, da tsohon shugaban kasar Alhaji Mahaman Ousman.
Kotun dai ta yi watsi da takarar Abdoulkarim Bakasso wanda jam’iyyar PDP Annur ta tsayar a matsayin nata dan takara, saboda a cewar Kotun takardun takararsa ba su cika ba.
Rahoto: An tantance 'Ya takara 15 a zaben Nijar na 2016
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu