Somalia

Sojin Amurka sun kai sabbin hare-hare kan Al-Shabaab

Dakarun da Amurka ta aike da su kasar Somalia a watan Afrilu na shekarar  2017 da muke ciki.
Dakarun da Amurka ta aike da su kasar Somalia a watan Afrilu na shekarar 2017 da muke ciki. Kacper Pempel / Reuters

Kasar Amurka ta kaddamar da sabbin hare-hare kan mayakan Al-Shabab a kasar Somalia, shi ne karo na biyu cikin wannan wata an Yuli.

Talla

Mai magana da yawun sojin Amurka dake kula da nahiyar Africa Patrik Barnes, ya ce nan gaba kadan zasu bayyana irin nasarorin da suka samu a harin da suka kai wa mayakan Al-Shabaab.

A cewar Barnes, burin Amurka shi ne taimakawa Somalia domin murkushe ‘yan kungiyar Al-Shabab don kasar ta sami kwanciyar hankali.

Tun a shekara ta 2007 Al-Shabaab da ke alaka da Al-Qa’eda ke fafutukar ganin ta hambarar da gwamnatin Somalia.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI