Amurka-Nijar

Tallafi zuwa yan gudun hijira a Diffa

'Yan gudun hijirar rikicin Boko Haram a Jihar Diffa
'Yan gudun hijirar rikicin Boko Haram a Jihar Diffa irinnews.org

Amurka ta bayyana bada tallafin dalla milyan 45 domin tallafawa yan gudun hijirar rikicin boko haram a yankin Diffa dake kudu maso gabashin jamhuriyar Nijar, kan iyakar kasar da tarayyar Najeriya, kamar yadda majalisar dinkin duniya ta sanar

Talla

A karshen watan yulin shekarar bara ne dai, gwamnatin jamhuriyar Nijar ta bukaci kasashen duniya da su tallafawa hukumar abinci ta Majalisar Dinkin Duniya PAM da kudi, bayyan da hukumar ta bayyana cewa zata dakatar da ayyukan tallafin da take ga yan gudun hijirar saboda rashin kudi.

To sai dai tuni masu sharhi kan ayyukan jinkai a kasar na bukatar ganin an zura ido sosai ta yadda tallafin zai kai ga mabukata.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI