Najeriya-Ilimi

Majalisar Najeriya na nazarin amincewa da sabbin Jami'o'i 80

kofar shiga tsohuwar Jami'ar Bayero University da ke Kano a Tarayyar Najeriya.
kofar shiga tsohuwar Jami'ar Bayero University da ke Kano a Tarayyar Najeriya. REUTERS/Stringer

Majalisar Dokokin Najeriya na nazari kan shirin amincewa da sabbin jami’oi da manyan kwalejin fasaha da kwalejojin ilimi 80 domin wadata kasar da manyan makarantu.

Talla

Rahotanni sun ce yanzu haka aiki yayi nisa domin ganin an amince da wadannan bukatu da suk afito daga sassa daban daban na kasar.

Tuni kungiyar malaman jami’oi ta soki shirin, inda ta bukaci Majalisar da ta mayar da hankali wajen ganin an samarwa jami’oin da ake da su isassun kudaden aiki.

Sai dai wasu na ganin matakin zai taimaka wajen saukakawa miliyoyin dalibai samun guraben karatu a matakan gaba da sakandire.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI