Amurka ta haramta Visa ga 'yan Najeriya masu karya tsarin dimokaradiya
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Ma’aikatar harkokin wajen Amurka tace ta kaddamar da wani shirin hana ‘yan Najeriya da ke yiwa dimokiradiya zagon kasa lokacin zaben shugaban kasa da ‘yan majalisu izinin shiga kasar.
Mai Magana da yawun ma’aikatar Morgan Ortagus, ta ce wadannan mutane sun aikata laifukan kama karya lokacin zaben da ya gabata da suka hada da take hakkin Bil Adama.
Ortagus ta ce shirin ya shafi wasu ‘yan siyasa ne, banda sauran ‘yan Najeriya da kuma zababbun shugabanin da ke gwamnati.
Sai dai sanarwar bata bayyana sunayen mutanen da haramcin shiga Amurkan ya shafa ba.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu