'Yan bindiga sun kashe mutane 8 a Najeria
Wallafawa ranar:
Bayanai daga Najeriya sun tabbatar da mutuwar mutane 8 cdiki har da sojoji uku, a harin da ‘yan Boko Haram suka kai kan sansanin soji da kuma wani kauye da ke jihar Borno.
Shaidu sun ce an kai hare-haren ne a ranar asabar da ta gabata a barikin soji da ke Gubio mai tazanar kilomita 80 daga Maiduguri inda suka kashe sojoji uku.
Fararen hula biyar ne suka rasa rayukansu a musayar wutar da aka yi tsakanin sojoji dan mayakan na reshen kungiyar Boko Haram da ake kira ISWAP.
Wadanda suka shaidi lamarin sun ce maharan sun zo ne a cikin motoci 8 da kuma manyan makamai, inda suka share tsawon awanni hudu ana musayar wuta.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu