A tarayyar Najeriya rashin jituwa tsakanin Sarkin Kano Muhammadu Sunusi na biyu da gwamnan jihar Abdullahi Umar Ganduje na kara fitowwa fili, ganin har ta kai jallin mahukuntan jihar sun sake gindaya masa wasu sabbin sharuda, ciki harda katse duk wata hulda ta kai tsaye da fadar gwamnati zuwa karamar hukuma abunda ya hada harda izinin yin balaguroTo domin shawo kan sabanin dai yanzu haka kungiyar dattawan arewacin kasar ta Northern elders forum, ta soma wani zama na sulhunta shugabannin biyu a birnin Kano.A cikin shirin Mu zagaya Duniya Garba Aliyu Zaria ya mayar da hankali zuwa wasu daga cikin manyen labaren mako.