Afrika

An killace wani dan kasar Jamus da ya kamu da Coronavirus a Masar

Wani dan kasar Jamus dake yawon bude ido a Masar ya zama mutumi na farko da ya mutu a Afirka sakamakon kamuwa da cutar coronavirus wadda yanzu haka ta razana kasashen duniya.

Wasu daga cikin jami'an kiwon lafiya dake yaki da zazzabi coronavirus
Wasu daga cikin jami'an kiwon lafiya dake yaki da zazzabi coronavirus REUTERS/Kim Kyung-Hoon
Talla

Hukumomin Masar sun bayyana mutumin a matsayin mai shekaru 60 wanda ya fara nuna alamun zazzabi lokacin da aka kwantar da shi a asibitin Hurghada ranar 6 ga watan nan.

Ma’aikatar lafiyar kasar tace mutane 45 ake zargin suna dauke da cutar, wadanda suka hada da yan kasa da bakin da suka kamu a wani jirgin ruwa.

Firaminista Mostafa Madbouli yace jirgin na dauke ne da mutane 171, wadanda suka hada da baki 101 da kuma 70 yan Masar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI