Coronavirus

Coronavirus ta yi kisan farko a Afrika

Kwayar cutar Coronavirus na haddasa murar mashako da ke sarke hanyar numfashi
Kwayar cutar Coronavirus na haddasa murar mashako da ke sarke hanyar numfashi MAM/CDC/Handout via REUTERS

Wani dan kasar Jamus da ke yawon bude ido a Masar ya zama mutum na farko da ya mutu a Afrika sakamakon kamuwa da cutar Coronavirus wadda yanzu haka ta razana kasashen duniya.

Talla

Hukumomin Masar sun bayyana mutumin a matsayin mai shekaru 60 wanda ya fara nuna alamun zazzabi lokacin da aka kwantar da shi a asibitin Hurghada ranar 6 ga watan nan.

Ma’aikatar Lafiyar kasar ta ce, mutane 45 ake zargin suna dauke da cutar, wadanda suka hada da 'yan kasa da bakin da suka kamu a wani jirgin ruwa.

Firaminista Mostafa Madbouli ya ce, jirgin na dauke ne da mutane 171, wadanda suka hada da baki 101 da kuma 70 'yan Masar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI