Gungun fasinjojin Gambia sun tsere daga inda aka killace su
Wallafawa ranar:
Jami’an tsaro da hukumomin lafiyar Gambia sun dukufa wajen neman wasu mutane 14 da suka tsere daga otal din da aka killace su, bayan zargin cewa sun kamu da cutar murar Coronavirus.
Gungun marasa lafiyar dai na daga cikin fasinjoji 32 da suka sauka a Banjul babban birnin kasar ta Gambia daga Birtaniya tun a larabar da ta gabata, wadanda a take aka killace su.
MInistan lafiyar Gambia Ahmadou Lamin Samateh yace ta karfin tsiya fasinjojin suka balle kofar shigar otal din kafin samun nasarar tserewa.
A talatar da ta gabata Gambia ta bada rahoton farko na bullar murar ta coronavirus a kasar bayan gano wata mata da ta kamu bayan isa kasar daga Birtaniya.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu