DRC-EBOLA

An kawo karshen Ebola a Jamhuriyar Congo- WHO

Hukumar Lafiya ta Duniya ta ce, an yi nasarar kawo karshen cutar Ebola wadda ta barke a karo na 10 a Jamhuriyar Demokradiyar Congo, yayin da ta jinjina wa gwamnatin kasar da sauran wadanda suka taimaka wajen yaki da cutar.

Sama da mutane dubu 2 suka mutu a sanadiyar cutar Ebola a Jamhuriyar Demokradiyar Congo
Sama da mutane dubu 2 suka mutu a sanadiyar cutar Ebola a Jamhuriyar Demokradiyar Congo REUTERS/Goran Tomasevic/File Photo
Talla

Duk da cewa, Hukumar Lafiya ta Duniya WHO ta yi jinjina ga wadanda suka bada gundunmawar kawar da cutar Eboba a Jamhuriyar Demokradiyar Congo, amma ta yi gargadin cewa, akwai bukatar ci gaba da sanya ido tare da agaza wa mutanen da suka kubuta daga annobar.

A cikin sanarwar da ta raba wa manema labarai ciki har da RFI Hausa, shugaban Hukumar Lafiyar ta Duniya, Tedros Adhanom Ghebreyesus ya ce, a halin yanzu duniya na da kayayyakin yaki da cutar ta Ebola kuma tuni aka bada lasisin riga-kafinta, sannan kuma an gano hanyoyin magance ta.

Shugaban Hukumar ta WHO ya ce, ya kamata a yi bikin wannan lokaci na kawo karshen cutar, amma kuma kar a kuskura a shantake saboda a cewarsa, kwayoyin cuta basa sassauci.

Sanarwar ta kara da cewa, babban riga-kafin barkewar duk wata annoba, shi ne zuba jari a ingantaccen tsarin kiwon lafiya.

A ranar 1 ga watan Agustan shekarar 2018 aka sanar da barkewar Ebola a Arewacin Kivu na Jamhuriyar Demokradiyar Congo, inda a jumulce aka samu asarar rayukan mutane dubu 2 da 287 daga cikin mutane dubu 3 da 470 da suka harbu da ita.

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da kasashen duniya ke fama da sabuwar cutar coronavirus, kuma darasin da aka dauka daga cutar Ebola na taimakawa wajen tunkarar Covid-19 a cewar sanarwar ta WHO.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI