Kamaru

Jagoran 'yan adawan Kamaru ya yi barazanar kifar da gwamnatin shugaba Biya

Jagoran ‘yan adawa a Kamaru Maurice Kamto, ya yi barazanar shirya zanga-zangar da za ta kawo karshen mulkin shugaba Paul Biya, matukar dai shugaban ya ce zai shirya zaben larduna ba tare da an cika wasu sharudda ba.

Maurice Kamto, jagoran 'yan adawan Kamaru
Maurice Kamto, jagoran 'yan adawan Kamaru MARCO LONGARI / AFP
Talla

Kamto, dan takarar jam’iyyar MCR a zaben shugabancin kasar da aka yi cikin 2018, a taron manema labarai da ya jagoranta a birnin Yaounde, ya ce dole ne a cika wadansu sharuda, da suka hada da samar da zaman lafiya da ‘yan aware, sannan a bude tattaunawa tsakanin gwmanati da sauran jam’iyyun siyasar kasar, idan ba haka ba kuwa zai jagoranci zanga-zangar da za ta kawo karshen mulkin shugaba Paul Biya.

A wannan karo dai Kamto, wanda ya zo na biyu ta fannin yawan kuri’a a zaben da ya gabata, ya ce ba ya da niyyar kaurace wa zaben lardunan kasar da za a yi nan ba da jimawa ba kamar yadda ya yi a zaben ‘yan majalisar dokokin kasar da aka yi cikin watan fabarairun da ya gabata.

A maimakon haka jagoran ‘yan adawar ya ce ba ta yadda za a shirya wani zabe a yanayin da kasar ta ke ciki a yau, kuma yunkurin shirya wani zabe zai kasance dalilin kawo karshen mukin shugaba Biya, kuma za a kawar da shugaban ne ta hanyar shirya tarzoma a kan titunan kasar a cewarsa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI