Faransa

Kungiyar Turai ta yi Allah wadai da harin da aka kai Faransa

Shugaban Faransa a garin Nice tareda rakiyyar Magajin Birnin Nice na kasar ta Faransa
Shugaban Faransa a garin Nice tareda rakiyyar Magajin Birnin Nice na kasar ta Faransa REUTERS/Eric Gaillard/Pool

Shugabannin Kungiyar Turai sun yi Allah wadai da harin da aka kai Faransa, inda suka bukaci kasashen duniya da su yi aiki tare wajen tattaunawa da fahimtar a tsakanin al’umma da kuma addinai maimakon rarrabuwar kawuna.

Talla

Sanarwar da shugaban Majalisar Turai Charles Michel ya gabatar tace shugabannin kasashen Turan 27 sun bayyana goyan bayan su ga Faransa amma kuma sun ki cewa komai dangane da cece kucen da ya biyo bayan zanen batuncin da ake yiwa addinin Islama.

Sanarwar tace su shugabannin Turai sun kadu da harin na Faransa, inda suka bukaci shugabannin kasashen duniya da su hada kai wajen tattaunawa da fahimtar juna.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI