Najeriya

Najeriya ta sake fadawa matsin tattalin arziki

Najeriya ta fada cikin matsin tatalin arziki a karo na biyu cikin shekaru 5 sakamakon annobar Covid 19 da faduwar farashin danyen mai, kamar yadda hukumar kididdiga ta kasar ta bayyana a ranar Asabar.

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari.
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari. © Nigeria Presidency/Handout via REUTERS
Talla

Kudaden shigar kasar a rubu’i na 3 a wannan shekarar ya yi kasa a karo na 2 a jere, da kashi 3 da digo 62, a cewar hukumar kididdiga ta kasar.

Hukumar ta dora alhakin haka a kan faduwar farashin danyen mai a kasuwannin duniya da kuma tasirin annobar coronavirus.

Kudaden shiga da ke da nasaba da danyen mai ya yi kasa da kusan kashi 14, idan aka kwatanta da kusan kashi 7 a rubu’i na 2, a cewar hukumar.

Asusun ba da lamuni na duniya ya yi hasashen cewa tattalin arzikin kasar zai rikito da sama da kashi 5 a wannan shekarar, amma gwamnatin kasar ta ce zai fadi da kusan kashi 9.

Najeriya, wacce ita ta fi samar da danyen mai a nahiyar Afrika, kafin yanzu, tana samar da ganga miliyan 2 ne duk rana, amma tasirin annobar covid 19 ya sa ta sauka zuwa ganga miliyan 1 da dubu dari 4.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI