'Yan Burkina Faso za su yi zabe a yanayi na matsalar ta'addanci

A  Lahadin nan al’ummar Burkina Faso za su kada kuri’a a zaben shugaban kasar a cikin yanayi na ta’azzara hare haren ‘ya ta’adda, zaben da ake kyautata zaton shugaba mai ci Roch Marc Christian Kabore zai samu galaba.

Wata rumfar zabe Ouagadougou na Burkina Faso.
Wata rumfar zabe Ouagadougou na Burkina Faso. AHMED OUOBA / AFP
Talla

Sai dai ba za a yi zabe a kashi daya cikin 5 na kasar ba, inda akasarinsa ya fita daga ikon gwamnatin kasar, kuma yake fuskantar hare haren mayaka masu ikirarin jihadi kusan kullayaumin.

Tashin hankalin ya tilasta wa mutane miliyan 1 barin gidajensu, wanda ke a matsayin kashi 5 na yawan al’ummar kasar miliyan 20, kuma mutane dubu 1 da dari 2 sun mutu tun daga shekarar 2015.

Matsalar tsaron ce ta mamaye yakin neman zaben na gobe Lahadi, inda kuma aka aike da dakarun da ba a bayyana adadinsu ba don tabbatar da tsaro aranar zaben.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI