Idriss Deby ya ziyarci Buhari a Abuja
Wallafawa ranar:
Shugaban kasar Chadi Idris Deby Itno ya ziyarci Najeriya inda ya gana da shugaban kasa Muhammadu Buhari kan batutuwan da suka shafi kasashen biyu.
Fadar shugaban Najeriya ba ta yi bayani kan abubuwan da shugabannin suka tattauna a Abuja ba, amma ziyarar Deby na zuwa ne a daidai lokacin da Najeriya da Nijar da Chadi da kuma Kamaru ke fuskantar karuwar hare-haren mayakan Boko Haram.
A makwanni biyu da suka gabata, hare-haren ta’addanci sun yi sanadiyar hallaka mutane sama da 200 a Jamhuriyar Nijar.
Shugaba Idris Deby da ya kwashe shekaru sama da 30 a karagar mulki yana takara a zaben da za’ayi ranar 11 ga watan gobe.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu