Guinea - Muhalli
Kasa ta rubza kan mahakan Zinare da dama a arewacin Guinea
Wallafawa ranar:
Mutane akalla 15 ne suka rasa rayukansu a yankin Siguiri dake arewa maso gabashin kasar Guinea, sakamakon rubzawar da ramin hakar zinaren da suke ciki yayi.
Talla
Masu aikin ceto sun ce hatsarin ya auku ne a kauyen Tatakourou sakamakon fadawar da wani dutse yayi kan gefen ramin hakar ma’adanan, sai dai ba a tantance ko dutsen ne ya danne mutanen ba, ko kuma kasar da ta rubza ce ta kashe su.
Makamancin wannan hatsarin dai ya taba aukuwa a kasar Guinea cikin watan Fabarairun shekarar 2019, abinda yayi sanadin mutuwar mahakan zinare 17.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu