Sin

Wani ya kashe kansa a Sin, ya raunata mutane shida

Saboda rashin gamsuwa da rashin adalcin da ya yi zargin ana nunawa, wani mutumin karkara a gabashin kasar Sin ya ta da bam a wani ginin karamar hukuma, inda ya kashe kansa ya kuma raunata mutane shida.

Shugaban kasar Sin, Hu Jintao
Shugaban kasar Sin, Hu Jintao 路透社
Talla

Mutumin wanda ake kira, Qu Huaqiang, rahotanni sun nuna cewa ya shigar da wata kara ne a rubuce, koda yake ba a fadi menene kokensa ba.

Haka kuma ba a tabbatar ko wadanda su ka ji raunukan ma’aikatan karamar hukumar ne ba.

Wani jami’i a garin Tengjia, ya tabbatarwa da Kamfanin Dillancin labaran AFP,da aukuwar lamarin, sai dai ya musanta cewa, Huaqiang ya shigar da wata kara a rubuce.

Tuni dai labarin ya bazu a yanar gizo inda ‘Yan kasar ke ta tofa albarkacin bakinsu kan lamarin.

Tattalin arzikin kasar ta Sin, duk da cewa ya bunkasa a cikin shekaru 30 da su ka wuce, ya janyo babban gibi tsakanin masu hanu da shuni da talakawan kasar.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI