Syria

Fararen hula 30 sun mutu a rikicin Syria

Wasu 'Yan tawayen kasar Syria
Wasu 'Yan tawayen kasar Syria Reuters/Goran Tomasevic

Akalla mutane 30 ne suka rasa rayukansu a jiya Alhamis bayan fashewar wani abu a wani gidan mai sakamakon harin da dakarun kasar Syria suka kai ta sama a yankin Arewacin kasar, kamar yadda kungiyoyin fararen hula suka sanar.

Talla

Mutane da dama ne su ka kuma jikkata a wajen da fashewar ta faru da ke Arewacin kauyen Ain Issa.

A daya gefen kuma ‘Yan tawayen kasar, sun bayyana kakkabo wani jirgin helicoptan sojan Syria a kusa da Damas, inda yan adawa suka bayyana cewa, mutane sun fice daga unguwarninsu sakamakon kazamin fadan da ake tabkawa.

Sai dai gidan talbijin na Kasar ya rawaito cewa, jirgin ya fadi ne bayan ya yi karo da wani jirgin farar hula.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI