China-Corona

China ta sanya dokar hana baki shiga sassanta har 'yan asalin kasar

Hukumomi a China sun hana ‘yan kasashen waje shiga kasar, yayin da kuma suka kudiri aniyar hana wadanda ke da biza da izinin zaman kasar izinin shiga kasar duk dai a wani mataki na dakile yiwuwar sake samun ta’azzarar cutar a kasar.

Shugaban China Xi Jinping da wasu manyan jami'an tsaron kasar.
Shugaban China Xi Jinping da wasu manyan jami'an tsaron kasar. Xie Huanchi/Xinhua/Reuters
Talla

Sauran matakan da aka dauka sun hada da rage yawan jiragen da ke tashi zuwa kasashen waje, da kuma rage yawan fasinjoji da jiragen ke kwashewa da kashi 75.

A ‘yan makonnin da suka wuce, yawan masu kamuwa da cutar coronavirus ya ragu a China, amma matsalar ta sake kunno kai bayan wasu da suka kamu da cutar sun isa kasar daga kasashen waje.

Kawo yanzu dai cutar ta corona ko kuma COVID-19 da ta samo asali daga China ta fantsama zuwa kasashe 182 inda ta hallaka mutane fiye da dubu 26 galibinsu a nahiyar Turai.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI