Saudiya

Sarki Napoleon na cikin musibun da suka hana aikin hajji

A ranar Laraba ake sa ran fara gudanar da aikin hajjin bana tare mahajjata kimanin dubu 10 kacal bayan mahukuntan Saudiya sun takaita adadin mahajjatan saboda annobar coronavirus.Ba a karon farko kenan ba da ake samun irin wannan tarnaki, domin kuwa tarihi ya nuna cewa, tashe-tashen hankula da musibu sun hana gudanar da aikin hajjin a shekarun baya.

Annobar coronavirus ta tilasta wa mahukuntan Saudiya daukar matakin kulle Masallacin harami
Annobar coronavirus ta tilasta wa mahukuntan Saudiya daukar matakin kulle Masallacin harami AFP
Talla

Tarihi ya nuna cewa, a shekarar 1798, an soke aikin hajji baki daya bayan Sarki Napoleon na Faransa ya mamaye yankin gabas ta tsakiya, lamarin da ya hana maniyata zuwa Saudiya domin sauke farali.

A karon farko a tarihin baya-bayan, an hana miliyoyin maniyata daga kasashen duniya zuwa Saudiyar saboda annobar coronavirus.

A bangare guda, an samu wasu jerin ibtila’o’i da suka mamaye aikin hajjin, inda a shekarar 2015, turmutsutsi ya yi sanadin mutuwar alhazai dubu 2 da 300, baya ga wata kugiyar gini da ta kashe fiye da mahajjata 100 bayan ta rikito.

A shekarar 2006, an samu wani turmutsutsin da ya kashe mutane 364 a Mina, yayin da ginin wani otel ya rufta tare da kashe mutane 76 duk dai a shekarar.

A shekarar 2004, wani turmutsutsin ya kashe mahajjata 251, inda makamancin wannan ibtila’in ya kashe jumullar mutane 46 a 2003 da 2001.

A 1998, fiye da mutane 118 ne suka mutu saboda turmutsutsin Mina. Sai kuma a shekarar 1997 da wata gobara ta kashe mutane 343.

Haka ma a 1994, wani turmutsutsin ya kashe mahajjata 270, yayin da a 1990, alhazai dubu 1 da 426 suka riga mu gidan gaskiya bayan na’urar bada iska ta karkashin kasa ta daina aiki.

A shekarar 1987, hukumomin Saudiya sun dakatar da wata haramtacciyar zanga-zangar da Iraniyawa suka gudanar, kuma an samu mutane fiye da 400 da suka mutu a wannan tarzoma.

A shekarar 1979, daruruwan ‘yan bindiga sun yi garkuwa da mahajjata a Masallacin Ka’aba, inda daga bisani aka samu asarar rayuka 153, yayin da a 1975, wata gobara ta kashe alhazai 200.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI