Libya

An Sami Baraka A Cigaba Da Kaiwa Libya Hare Hare

Rahotanni  sun nuna cewar, an fara samun baraka tsakanin kasashen dake goyan bayan kai hare hare ga kasar Libya, inda kasar Italy da tayi alkawarin bada jiragen ruwan yaki takwas, take cewa, ita bata goyi bayan kaddamar da yaki kan Libya ba, kamar yadda Ministan harkokin wajen kasar, Franco Frattini ya bayyana.Wanann matsayi yayi dai dai da na kasar Jamus, inda Ministan harkokin wajen ta, Guido Westerwelle yace, sun yi nazarin hatsarin dake cikin aikin, kafin suka dauki matsayin rashin amincewa.Fira Ministan kasar Britaniya David Cameron yace ba haka abin yake ba. 

Daya daga cikin hare hare da aka kaiwa Libya
Daya daga cikin hare hare da aka kaiwa Libya rfi
Talla

Jawabin da Fira Ministan Britania David Cameron yayi

''Wannan shiri ne na kare mutane, da kuma baiwa mutanen Libya dama su tsarawa kansu abinda suke so.''

 

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI