Wole Soyinka Zai Kafa Jamiyyar Siyasa
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Shahararren marubucin nan dake Najeriya Farfesa Wole Soyinka wanda ya taba samun kyautan Nobel na gwanancewa wajen rubuce-rubuce ya bayyana shirin sa na kafa jamiyyar Siyasa.A tattaunawa da sashen Hausa na Radiyo Faransa- RFI, Farfesa Wole Soyinka bai ce ga ainihin sunan jamiyyar siyasar ba tukuna.Shi dai Farfesa Wole Soyinka na bukukuwan cikan sa shekaru 76 ne yana raye a duniya.A cewar sa ba wannan ne karonsa na farko ba daya shiga jamiyyar Siyasa domin cikin janhuriya ta biyu ya kasance dan jamiyyar PRP ne tare da Balarabe Musa.Yace a wancan lokaci har ya riki wani mukami karami cikin jamiyyar.Yace a koda yaushe ya kan bada goyon bayan sa ga jamiyyar da take da manufofi masu kyau.Ta haka ne yace zaa yaki raayoyi marasa amfani ga jamaa.