WHO

Hukumar lafiya ta duniya tace an samu raguwar matuwar yara

Najeriya tana cikin kasashe da ke fama da ciwon Bakon Dauro
Najeriya tana cikin kasashe da ke fama da ciwon Bakon Dauro Mike Blyth/ domaine public

Hukumar lafiya ta duniya, WHO, ta bayyana cewa, an samu raguwar mace-macen yara kanana, da ciwon Bakon Dauro ke kashewa a duniya, da fiye da kashi 70 cikin dari a shekaru goma da suka gabata. Hukumar, tace hakan yana da nasaba da irin cigaban da aka samu ta fannin karuwar magungunan cutar.