Najeriya

An mallakawa gwamnati motocin Dikko Inde

Wata kotu dake Kaduna a Najeriya ta bada umarnin wucin gadi na mallake motocin kasaita 17 da aka gano a gidan tsohon shugaban hukumar kwastam Abdullahi Dikko Inde.

Abdullahi Dikko Inde ya yi murabus daga mukaminsa na shugaban hukumar kwastam a shekarar 2015
Abdullahi Dikko Inde ya yi murabus daga mukaminsa na shugaban hukumar kwastam a shekarar 2015 Daily trust
Talla

Mai shari'a SM Shuaibu na Babbar kotun tarayya dake Kaduna ya bada umurnin kamar yadda Hukumar EFCC ta bukata.

Alkalin ya ce an mallakawa gwamnatin Najeriya wadannan motoci 17 wadanda za'ayi amfani da su a matsayin shaida a tuhumar da ake yiwa tsohon shugaban kwastam na halarta kudaden haramun.

A wannan makon ne Hukumar da ke Yaki da cin hanci da rashawa a Najeriya ta EFCC ta sanar da kwace motoci 17 na kasaita daga hannun tsohon shugaban hukumar kwastam.

Mai Magana da yawun hukumar Wilson Uwujeran yace an gano motocin ne a wani gida da Dikko ya mallaka dake Kaduna sakamakon bayanan da suka samu cewar an boye kudi da dukiyar sata a ciki.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI