Najeriya

'Yan kunar bakin wake sun mutu a Maiduguri

Maharan kunar bakin wake na kai hari jifa-jifa a jihar Borno da ke Najeriya
Maharan kunar bakin wake na kai hari jifa-jifa a jihar Borno da ke Najeriya AFP PHOTO

Wasu wata uku maharan kunar bakin wake sun rasa rayukanu bayan daya daga cikinsu ta tada bam din da ke jikinta a kusa da wasu tankokin mai a safiyar yau a birnin Maiduguri na jihar Borno da ke arewa maso gabashin Najeriya.

Talla

Tankokin man guda biyu da aka ajiye su akan hanyar Damboa sun kone kurmus sakamakon aukuwar lamarin.

Mai magana da yawun hukumar bada agajin gaggawa a yankin arewa maso gabashin Najeriya, Abdulkadir Ibrahim, ya ce, tuni aka kwashe gawarwakin maharan na kunar bakin wake.

Ibrahim ya ce, an kuma shawo kan gobarar da tashin bam din ya haddasa, yayin da wasu majiyoyi ke cewa, harin bai shafi  jama'a ba.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI