Najeriya-Boko Haram

Najeriya: Matan da Boko Haram ta sace sun nemi agajin Gwamnati

Wasu daga cikin matan da mayakan Boko haram suka sace a jihar Borno, ranar 17 ga watan Yuni 2017.
Wasu daga cikin matan da mayakan Boko haram suka sace a jihar Borno, ranar 17 ga watan Yuni 2017. Sahara Reporters

Kungiyar Boko Haram ta fitar da wani sabon hoton bidiyo, da ke nuna wasu mata da ta sace a jihar Borno.

Talla

Matan dai sun roki gwamnatin Najeriya da ta tattauna da mayakan, domin a sako su.

Matan na daga cikin wadanda mayakan Boko na Boko Haram suka sace, yayinda suke kan hanyarsu ta zuwa garin Damboa daga garin Maiduguri a ranar 17 ga watan Yunin da ya gabata, yayinda jami’an tsaro ke musu rakiya.

A lokacin da mayakan sukai wa tawagar motocin kwanton Bauna, sun hallaka wasu daga cikin jami’an tsaron da ake wa rakiya zuwa wuraren aikinsu a garin na Damboa.

Najeriya: Matan da Boko Haram ta sace sun nemi agajin Gwamnati

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI