Najeriya

Boko Haram ta dirar wa sojojin Najeriya da asuba

Rahotanni daga jihar Bornon Najeriya na cewa, mayakan Boko Haram sun kashe mutane da dama da suka hada da jami'an tsaro a wani farmakin ba-zata da suka kai sansanin sojin kasar a sanyin safiyar wannan Larabar.

Wasu daga cikin mayakan Boko Haram
Wasu daga cikin mayakan Boko Haram pmnewsnigeria
Talla

Mayakan sun taso ne daga Gwoza Kalla domin kai harin a kan dakarun kasar da ke garin Damboa da misalin karfe 5:30 na asuba agogon Najeriya,inda suka yi ta ruwan harsashai kan sansanin.

Wani ganau ya ce, mayakan sun yi amfani da manyan motocin yaki guda biyu, yayin da suka yi ta harbe-harbe lokaci zuwa lokaci.

Bayanai na cewa, an shafe tsawon sa’o’i biyu ana dauki-ba-dadi da mayakan na Boko Haram.

A yanzu dai hankula sun kwanta, amma tuni jama’a da dama suka tsere zuwa garin Chibok don samun mafaka.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI