Najeriya

Gwamnatin Ganduje ta tsige Sarkin Kano daga karaga

Gwamnatin Kano da ke Najeriya ta tsige Sarkin Kano, Alhajji Muhammadu Sanusi na II daga karagarsa saboda rashin mutunta ofishin gwamna da sauran hukumomin gwamnatin jihar kamar yadda gwamnatin ta ce.

Sanusi Lamido Sanusi tare da gwamnan Kano, Abdullahi Umar Ganduje
Sanusi Lamido Sanusi tare da gwamnan Kano, Abdullahi Umar Ganduje Dandago RFI
Talla

Sakataren gwamnatin jihar, Alhaji Usaman Alhaji ya ce, tsigewar za ta fara aiki nan take .

Sakataren ya ce, ayyukan Sarkin sun saba wa kashi na 3, sashi na A-E na dokokin jihar Kano, abin da ya sa aka tsige shi.

A cewar sakataren, sun tuntubi masu ruwa da tsaki kafin daukar matakin tsige Sarki Sanusi, yana mai cewa, nan kusa za a sanar da sabon sarkin da zai gaji Sanusi.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI