Gwamnan Kaduna ya baiwa tsohon Sarkin Kano mukami
Gwamnatin jihar Kaduna dake Najeriya ta nada tsohon Sarkin Kano Muhammadu Sanusi na II a matsayin mataimakin shugaban majalisar gudanarwar hukumar zuba jari ta Jihar kwana guda bayan tube shi daga Sarautar Kano.
Wallafawa ranar:
Gwamnan Jiahr Malam Nasir El Rufai ya sanar da nada shugabannin hukumar a karkashin jagorancin mataimakiyar Gwamnan Jihar Dr Hadiza Balarabe domin ganin sun taimaka wajen janyo hankalin masu zuba jari zuwa jihar.
El Rufai ya bayyana fatar sa na ganin Jihar Kaduna ta mafana daga ilimi da kwarewar Sarkin da kuma irin mutanen da ya sani a kasashen duniya.
Gwamnan ya yabawa wakilan kwamitin gudanarwar saboda amincewa su yiwa jihar aiki.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu