'Yar Buhari ta killace kanta bayan komawa Najeriya daga Turai
Wallafawa ranar:
Uwargidan Shugaban Najeriya Aisha Buhari ta sanar da cewar an killace daya daga cikin ‘yayan shugaban kasa Muhammadu Buhari da ta koma kasar daga Birtaniya saboda kaucewa kamuwa da cutar coronavirus.
Aisha Buhari ta sanar da haka ne a sakon twitter da ta aike, inda take cewar ‘yar ta su bata nuna aalamun kamuwa da cutar ba, sai dai sun dauki matakin ne sakamakon shawarar da kwamitin yaki da cutar ya ba su.
Uwargidan shugaban tace ta yanzu haka ta rufe ofishin ta na makwanni biyu inda ta bukaci ma’aikatan ta su dinga aiki daga gidajen su, yayin da ta yabawa gwamnonin arewa maso yamma da suka rufe makarantu domin kare dalibai.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu