Najeriya

Likitocin Najeriya na yajin aiki a yayin da Coronavirus ke barna

Kungiyar Likitocin Najeriya ta bai wa ‘yayanta da ke yajin aiki a wasu jihohin kasar da su gaggauta komawa bakin aiki domin taimaka wa gwamnati wajen dakile yaduwar cutar Coronavirus.

Wasu jami'an kiwon lafiya sanye da rigunan kariya daga cuta mai yaduwa
Wasu jami'an kiwon lafiya sanye da rigunan kariya daga cuta mai yaduwa REUTERS/Baz Ratner
Talla

Shugaban Kungiyar Francis Faduyile ya bayyana haka a birnin Abuja, inda ya ce, shugabannin kungiyar na kasa za su karbe tattaunawa da rassan kungiyoyin da ake takun-saka domin warware matsalar.

Faduyile ya bukaci gwamnatin Najeriya ta gaggauta samar da isassun kayan aiki ga ma’aikatan lafiyar da ke fuskantar wannan matsala ta kula da masu dauke da cutar.

Kungiyar ta kuma bukaci samar da wurare masu kyau da za a rika killace wadanda aka gano dauke da cutar.

Ya zuwa yanzu Kungiyar Likitocin rassan Abuja da Gombe da Enugu da Kaduna da kuma Cross Rivers ke yajin aiki.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI