Bakonmu a Yau
Masana kimiyya a Najeriya sun shawarci hukumomi su rufe iyakoki don dakile yaduwar coronavirus
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:28
Kungiyar masana kimiyar Najeriya ta bukaci gwamnatin Kasar da ta gaggauta rufe iyakokin ta na makwanni hudu domin hana masu dauke da cutar coronavirus kutsa kai cikin kasar da kuma gano wadanda suke dauke da ita domin kula da su.Shugaban kungiyar Farfesa Mosto Onouha ya bayyana haka a sanarwar da ya rabawa manema labarai.Farfesa Balarabe Sani Garko na Jami’ar Ahmadu Bello dake Zaria, yayi tosakaci a kan wannan batu a tattunawarsa da Bashir Ibrahim Idris.