Najeriya

Dokar hana fita ta fara aiki a Lagos da Abuja

Al’ummomin Lagos, Abuja da Ogun a Najeriya, sun share daren farko zaune a gidajensu, bayan da dokar hana fita tsawon makonni biyu ta fara aiki da misalin karfe 11 na daren da ya gabata don hana yada cutar Coronavirus.

Filin jirgin sama na Murtala Muhammed da ke Lagos
Filin jirgin sama na Murtala Muhammed da ke Lagos REUTERS/Akintunde Akinleye
Talla

Adadin wadanda suka kamu da cutar a Najeriya ya tashi zuwa 131  bayan da aka samu karin mutane 20 da suka kamu da ita a ranar Litinin, yayin da adadin wadanda suka rasa rayukansu ya tashi zuwa biyu a fadin kasar.

Alkalumman Cibiyar Yaki da Cututtuka ta kasar sun nuna cewa, an samu karin mutanen ne a jihohin Lagos, Kaduna, Oyo da kuma Abuja

Kamar yadda alkalumman cibiyar suka nuna, a jihar Lagos kawai an samu mutane 13, sai 4 a Abuja, 2 a Kaduna yayin da aka samu mutum daya a jihar Oyo, yayin da wasu bayanai ke cewa wanda aka sama a Oyo ba wani ba ne face gwamnan jihar Seyi Makinde.

Kafin samun karin wadannan mutane 20 a jiya, dama akwai mutane 111 da ke dauke da kwayar cutar ta Covid-19 a jihohin Lagos, Abuja, Ogun, Kaduna, Oyo, Edo, Bauchi, Enugu, Osun, Ekiti, Rivers da kuma Benue.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI