Najeriya

'Yan fashi sun kashe 'yan sanda 8 a Najeriya

Ana ci gaba da gudanar da bincike game da harin 'yan fashi a jihar Kogin Najeriya
Ana ci gaba da gudanar da bincike game da harin 'yan fashi a jihar Kogin Najeriya REUTERS/Afolabi Sotunde

Bayanai daga Najeriya na cewa, wasu gaggan 'yan fashi dauke da muggan makamai sun kashe jami'an 'yan sanda 8 cikinsu har da mai mukamin DPO bayan sun afka wa bankin First Bank da ke garin Isanlu a jihar Kogi.

Talla

Har ila yau, wata mata ta rasa ranta sakamakon harsashin bindiga da ya same ta a yayin musayar wuta tsakanin 'yan fashin da jami'an 'yan sandan a cewar rahotanni.

Kawo yanzu babu cikakken bayani game da lamarin da kuma adadin rayukan da suka salwanta, amma an ce, barayin sun kashe hatta wasu daga cikin ma'aikatan bankin da kwastamominsu.

Yanzu haka rundunar 'yan sanda ta dukufa wajen gudanar da cikakken bincike kafin ta yi karin bayani game da lamarin.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI