Najeriya

Sojin Najeriya sun halaka kwamandojin Boko Haram a Borno

Rundunar sojin Najeriya ta ce dakarunta sun yi nasarar halaka wasu kwamandojin mayakan Boko Haram, yayin gumurzun da suka yi a jihar Borno.

Wasu dakarun sojin Najeriya a Damboa, dake Najeriya.
Wasu dakarun sojin Najeriya a Damboa, dake Najeriya. STEFAN HEUNIS / AFP
Talla

Ma’aikatar tsaron Najeriya ta ce, dakarun sojin sun kaiwa mayakan samame ne a kan iyakar najeriya da Kamaru, lokacin da suke kokarin tsallakawa zuwa dajin Sambisa.

Sanarwar tace sojin Najeriyar sun kuma yi nasarar kwace makamai, tarin alburusai, Mota da kuma kekuna.

Ma’aikatar tsaron Najeriya ta ce daga cikin manayan kwamandojin na Boko Haram akalla 8 da ta halaka akwai, Ba Issoufou da ake kira da Tumbun Dabino, Amir Batam/ Tumbun Bororo da kuma Koukar Kowa/Tumbun Dila.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI