An sake kaiwa Zulum hari kasa da sa'o'i 24 bayan harin farko
An sake kaiwa tawagar motocin Gwamnan Jihar Barno dake Najeriya, Farfesa Babagana Umara Zulum hari, kasa da sa’oi 48 bayan wanda aka kai masa akan hanyar zuwa Baga wanda yayi sanadiyar hallaka akalla mutane 30.Wannan lamari ya sa wasu 'yan yankin kira ga gwamna Babagana Zulum da ya takaita tafiye-tafiye wasu yankunan jihohin dake barazanar hare-haren na Boko Haram domin kare lafiyar sa da sauran tawagarsa, duk kuwa da cewa tafiye-tafiyen nasa masu alfanu ne ga al'ummar yankin.Kuna iya latsa alamar sauti dake kasa don jin rahoto daga wakilin mu dake Maiduguri Bilyaminu Yusuf.
Wallafawa ranar:
An sake kaiwa tawagar Zulum hari
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu