Najeriya

Mun yi wa Boko Haram luguden wuta-Sojin Najeriya

Jirgin yakin sojojin saman Najeriya
Jirgin yakin sojojin saman Najeriya Nigerian Monitor

Shalkwatan Tsaron Najeriya ya bayyana cewa, dakarunsa na Operation Lafiya Dole sun sake samun nasarar fatattakar mayakan Boko Haram a sansanoninsu da ke yankin arewa maso gabashin kasar.

Talla

Jami’in Yada Labaran Shalkwatan, Manjo Janar John Eneche ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da ya fitar yau Asabar a birnin Abuja.

Jami’n ya ce, a ranar 1 ga watan Oktoban nan, sojojin suka fatattaki mayakan daga maboyarsu ta Maima da Tusuy da ke kusa da Warshale da kuma Tongule a jihar Borno.

Dakarun sun yi amfani da jiragen sama na yaki wajen kaddamar da farmaki kan mayakan na Boko Haram a cewar sanarwar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI