Najeriya

Najeriya ta rushe rundunar SARS mai yaki da fashi da makami

Sufeto Janar na 'yan sandan Najeriya, Muhammadu Adamu ya sanar da rusa rundunar da ke yaki da 'yan fashi da makami da ake kira SARS, sakamakon zanga zangar da aka gudanar saboda kaucewa ka’idar aiki.

Jami'an 'yansandan Najeriya.
Jami'an 'yansandan Najeriya. REUTERS/Afolabi Sotunde
Talla

Babban Sufeton yayin wani jawabin  kai tsaye ta gidan talabijin mallakin kasar, ya amsa kiran 'yan Najeriyar wajen rusa sashen rundunar ‘yansandan na musamman mai yaki da fashi da makami, yayinda ya bukaci gaggauta janye ilahirin jami'an na SARS da yanzu haka ke bakin aiki.

Mutane da dama da sun bayyana bacin ran su da yadda wasu batagari dake cikin rundunar ke azabtar da jama’a da raba su da dukiyoyin su da kuma kisa a wasu lokuta.

Al'ummar kasar dai sun shafe kwanaki suna zanga-zangar bukatar kawo karshen rundunar ta SARS wadda ta samu goyon bayan fitattu daga sassa daban-daban.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI