Ana cigaba da yiwa jama'a allurar yakar cutar Covid 19 a Najeriya
Wallafawa ranar:
A Najeriya kusan makonni uku da soma yiwa jama’a allurar rigakafin cutar Covid 19,alkaluma daga hukumar yaki da cuttuka ta kasar na nuni cewa mutane 374.585 ne suka amfana da wannan allura.
Jihar Kogi kadai ce yanzu haka ba a isa da wannan allura ba ,Faisal Shuaib dake shugabantar wannan hukuma ya bayyana cewa ana cikin gyaran dakin ajiye maguguna na jihar ta Kogi,dakin da masu zanga- zanga End Sars suka lallata a baya.
Cutar ta Covid 19 ta hallaka akala mutane 2000 a Najeriya, Jihar Lagas da aka fi yawan mutanen da suka kamu da wannan cuta,kusan mutane 92.000 suka amfana da wannan allura,jihar Ogun mutane 36.953, Bauchi 31.321, Kaduna 29.426, Jigawa 22.420 sai Kwara mutane 20.060.Jihohin dake da karancin mutane da suka amfana da wannan allura sun hada da Kebbi mutun daya,Taraba mutun guda sai Abia mutun daya.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu