Najeriya

Najeriya na shirin sake karbo bashin fin dala biliyan 4 a ketare

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya nemi majalisar dattawan kasar ta amince da ciwo karin bashin dala biliyan 4 da kuma euro miliyan 710 daga waje.

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari.
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari. AP - Bayo Omoboriowo
Talla

Kudurin na kunshe ne a cikin wasikar da shugaban ya aike wa shugaban Majalisar Dattawa Ahmad Lawan, wadda kuma aka karanta a zauren majalisar a yau Talata.

Buhari ya ce za a karbo rancen ne daga Bankin Duniya da Hukumar tallafawa ci gaban kasashe ta Faransa da kuma Bankin EXIM da ke Amurka da kuma Asusun Tallafawa Noma na Duniya IFAD.

Shugaban Najeriyar ya ce rancen zai bai wa Gwamnatinsa damar aiwatar da muhimman ayyukan raya kasa a sassa daban-daban.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI