Nijar

An sake bude jami’ar Yamai a yau Lahadi

Dalibi guda ya rasa ransa a boren da ya gudana a jami'ar Yamai.
Dalibi guda ya rasa ransa a boren da ya gudana a jami'ar Yamai. actuniger

Mako daya bayan rufe jami'ar Yamai dake Jamhuriyar Nijar, saboda boren dalibai, gwamnatin kasar ta sake bude jami'ar a yau Lahadi biyo bayan koken jama’a.

Talla

Ministan Ilimi Muhammad Bin Oumar ya fadi cikin wata sanarwa cewa matakin sake bude Jami'ar na zuwa ne saboda koke daga jama’ar dake bukatar a sake bude Jami’ar.

Sanarwar na cewa Shugaban kasar Mahammadu Issoufou ya gana da kungiyoyin daliban Jami’ar domin yi musu hudubar tattalin zaman lafiya.

A halin da ake ciki rundunar ‘yan sandan kasar ta ce ana tsare da dalibai uku wadanda ake zargin suna da hannu a rikicin da ya haddasa mutuwar dalibi daya.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI