Nijar

Mutum na 3 ya kamu da cutar Coronavirus a Nijar

Hukumomin Jamhuriyar Nijar sun sanar da samun mutum na 3 da ya kamu da cutar coronavirus bayan gano wata mata ‘yar kasar Brazil dake dauke da ita.

Ministan Lafiyar Jamhuriyar Nijar Dakta Iliyasu Idi Mainasara.
Ministan Lafiyar Jamhuriyar Nijar Dakta Iliyasu Idi Mainasara. RTI
Talla

Rahotanni sun ce matar ta shiga Nijar ne a ranar 16 ga wata daga Switzerland kuma tuni aka dauki matakin kula da ita.

Gwamnatin Nijar ta bayyana mayar da otel Gawai mai gadaje sama da 200 da Village Chinuwa mai gadaje sama da 100 a matsayin inda za’a killace masu dauke da cutar.

Fira ministan Briji Rafini ya ziyarci wuraren tare da likitoci domin ganin shirin da akayi.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI