Nijar

'Yan bindiga sun tarwatsa 'yan gudun hijira a Nijar

Wasu daga cikin 'yan gudun hijira
Wasu daga cikin 'yan gudun hijira REUTERS/Luc Gnago

Rahotanni daga Jamhuriyar Nijar na cewa dubban mutane ne suka tsere daga sansanin ‘yan gudun hijira da ke Intikane a cikin jihar Tawa gab da iyakar kasar da Mali, bayan da ‘yan bindiga suka kai hari tare da kashe mutane a kalla 3 a ranar Lahadin da ta gabata.

Talla

Ofishin Hukumar Kula da 'Yan Gudun Hijira na Majalisar Dinkin Duniya da ke Nijar ya ce, yanzu mutane dubu uku da suka tsere sun samu mafaka a garin Tlemces mai tazarar kilomita 27 daga sansaninsu na farko.

A kalla dai ‘yan asalin kasar Mali dubu 20 ne ke rayuwa a sansanin da aka kai wa harin, tare da wasu dubbai ‘yan Nijar da suka guje wa tashe-taashen hankulan da ake fama da su

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI