Nijar: Mutane 14 sun mutu a kusa da iyakar Mali sakamakon harin ta'addanci
Wallafawa ranar:
Ma’aikatar cikin gidan jamhuriyar Nijar ta tabbatar da mutuwar fararen hula 14 a harin da ‘yan bindiga a kan babura suka kai ranar shekaranjiya lahadi a wani kauye mai suna Wiye da ke gundumar Banibangou kusa da iyakar kasar da Mali.
Sanarwar ma’aikatar cikin gidan wadda aka fitar a yammacin jiya, ta ce 9 daga cikin mutanen an kashe su ne lokacin da suke noma a gonakinsu, 3 a cikin garin na Wiye sai kuma biyu wadanda maharan suka bindige a hanyarsu ta komawa gida daga gona.
Ma’aikatar cikin gidan ta kara da cewa an tsaurara matakan tsaro, kuma ana ci gaba da bincike don gano wadanda suka aikata aika-aikar da zummar gurfanar da su gaban kuliya.
Banibangou na cikin inda aka sani a matsayin yankunan iyakoki 3 tsakanin Nijar, Burkina Faso da Mali, wanda tsawon shekaru kef ama da munanan hare hare daga kungiyoyin mayaka masu ikirarin jihadi da ke da alaka da Al-Qaeda da IS.
A tsakiyar watan Maris, wasu da ake zargi masu ikirarin jihadi ne sun kai hari a wannan wurin, a kan wata kasuwa, lamarin da ya yi sanadin mutuwar mutane 66.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu