Tattaunawar Bashir Ibrahim Idris da Farfesa Umar Pate kan sadarwa
Wallafawa ranar:
Sauti 03:57
An bude taron masana sadarwa na Jami'ar Bayero da ke Kano a Tarayyar Najeriya, taron da ya mayar da hankali kan yada labarai da harsunan gida wanda ya samu halartar masana daga ciki da wajen kasar. Editan RFI Hausa da ke halartar taron ya tattauna da mataimakin shugaban jami'ar Kashere Farfesa Umar Pate Kaigaman Adamawa dangane da abin da taron ya kunsa.