Lafiya Jari Ce: Bullar wata lallura a jihar Kano bayan ta'ammali da lemo
Wallafawa ranar:
Sauti 09:58
A cikin shirin 'Lafiya Jari Ce' na wannan mako, Azima Bashir Aminu ta duba matsalar bullar wata lallurar rashin lafiya da ta addabi jihar Kano ta Najeriya, biyo bayan wani lemo da wasu mutane suka sha, lamarin da ya haddasa zazzabi mai zafi tare da fitsarin jini. Ya zuwa yanzu, mutane sama da 350 ne wannan lallurar ta shafa.