Birtaniya

Kotun birnin London ta tabbatar da belin Assange shugaban shafin WikiLeaks

Julian Assange shugaban shafin Wikileaks mai wallafa bayanan sirri da ya samu
Julian Assange shugaban shafin Wikileaks mai wallafa bayanan sirri da ya samu Reuters

A wani zama na tsawon mintina 90 a yau Alhamis madaukakiyar kotun birnin Landon ta kasar Birtaniya, ta bada bellin karar da a ka daukaka, ga shugaban shafin yanar gizon Wikileaks Mai fallasa bayanan sirrin da a ka bashi Julian Assange.Alkalin mai shara’a Duncan Ouselay, ya bayyana cewa, ya bada bellin Julian Assange bisa sharadi jinginar da kimanin Euro dubu 280. Matakin da ba za a daukaka kara a kansa ba.A ranar 7 ga watan nan ne, aka kama Julian Assange dan kasa Austarliya mai shekaru 39 a duniya, bisa bukatar kasar Sweden, dake son mika mata shi domin fuskantar hukumci kan zargin aikata faide a kasar wa wasu mata biyu.